1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAmurka

NATO: Scholz ya yi maraba da girke makamai a Jamus

July 11, 2024

Shugaban na gwamnatin Jamus ya nuna farin ciki kan matakin na Amirka inda ya ce abu ne da zai samar da zaman lafiya.

https://p.dw.com/p/4iC3p
Shugaban Amirka Joe Biden tare da shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz a taron NATO na 2024
Shugaban Amirka Joe Biden tare da shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz a taron NATO na 2024Hoto: Kay Nietfeld/dpa/picture alliance

Shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz, ya yaba wa matakin da Amirka ta dauka na girke makamai masu linzami da ke cin dogon zango a kasarsa domin nuna turjiya.

Olaf Scholz ya fada wa manema labarai a taron NATO da ake rufewa ranar Alhamis cewa abu ne na tabbatar da zaman lafiya da nuna turjiya sannan mataki ne mai muhimmanci a lokaci mafi dacewa.

Sabon firaminista ya yi alkawarin sake gina kasar

A ranar Laraba ce Amurka ta sanar da matakin karfafa NATO a Tarayyar Turai akan Rasha, ta hanyar fara girke manyan makamai masu linzami da ke cin dogon zango a Jamus daga 2026.

A martanin da ta yi kan matakin a wannan Alhamis, Rasha ta ce ta na shirin daukar matakin da ya dace domin dakile barazanar NATO.

Taron NATO na kwanaki uku yana gudana ne a kasar Amirka daidai lokacin da kungiyar tsaron ke cika shekaru 75 da kafuwa, inda yanzu take da mambobi 32, kuma take zama kawancen tsaro mafi girma da tasiri a duniya.