1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ana cigaba da laluben hanyoyin sulhunta rikicin Afghnistan

Zulaiha Abubakar
September 3, 2019

Sakataren kungiyar tsaro ta NATO Jens Stoltenberg ya bayyana cewar kungiyar za ta cigaba da bayar da goyon bayanta a kawo karshen rikici tsakanin 'yan Taliban da gwamnatin Afghanistan.

https://p.dw.com/p/3OwiI
Brüssel Jens Stoltenberg, NATO-Generalsekretär
Hoto: picture-alliance/Anadolu Agency/D. Aydemir

Tuni shugaba Donald Trump na Amirka ya sanar da shirin janye sojoji da yawansu ya kai dubu 8,600 daga kasar idan aka cimma daidaito a sulhun, an dai kwashe fiye da shekara guda tsakanin Amirka da Taliban ana laluben hanyoyin magance rashin jituwar da ke haifar da asarar rayuka da dukiyoyin gwamnati a Afghanistan.


Sakataren kungiyar tsaron ta NATO Jens Stoltenberg ya gana da shugabar hukumar zartarwar kungiyar tarayyar Turai Ursula von der Leyen a birnin Brussels game da batutuwan da suka shafi alakar kasashen ketare.