1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutuwar karin mutane a Siriya

November 10, 2011

Akalla mutane 12 suka hallaka a cigaba da dauki ba dadin da ke gudana tsakanin jami'an tsaro da masu bore a Siriya

https://p.dw.com/p/138KE
Shugaban kasar Siriya Bashar al-AssadHoto: picture-alliance/dpa

Aƙalla mutane 12 suka rasa rayukansu a ƙasar Siriya a cigaba da farmakin da sojoji ke kaiwa masu zanga-zangar neman sauyi. Ƙungiyoyin kare haƙƙin bil Adama da suka bada wannan labari sun ce wadanda suka muntun sun haɗa da wata 'yar ƙaramar yarinya guda da kuma sojoji shidda.

A ɗaya hannun ƙungiyoyin ƙwadago sun shiga yajin aikin gama gari a yankin Jabal al-Zaouiya domin nuna adawa ga matakain da gwamnatin ke ɗauka kan masu zanga-zanga.

A halin da ake ciki kuma, komitin da 'yan adawa suka girka na cigaba da rangadi a ƙasashen yankin Golf domin samun goyan baya ga buƙatarsu ta gurfanar da hukumomin Siriya gaban kotun ƙasa da ƙasa mai hukunta manyan lafukan yaƙi.

Wani rahoton Majalisar Ɗinkin Duniya ya bayyana cewar daga farkon rikicin Siriya zuwa yanzu fiye da mutane 3.500 su ka rasa rayukansu.

Mawallafiya: Pinado Abdu

Edita:           Usman Shehu Usman