1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar IS ta dauki alhakin harin Afghanistan

November 2, 2020

Alkaluman wadanda suka jikkata da kuma wadanda suka rasa rayukkansu na kara hauhawa sanadiyar harin ta'addanci da aka kai a wata Jami'ar a Kabul.

https://p.dw.com/p/3kmTq
Afghanistan Kabul Anschlag auf Universität
Hoto: Rahmat Gul/picture alliance/AP Photo

 

Bayan kwashe sa'oi ba a san wadanda suka kai harin ba, amma daga bisani Kungiyar IS ta dauki alhakin kai farmaki. Dama can kungiyar Taliban ta baiyana cewa ba tada hannu a harin.

Mai magana da yawun ma'aikatar cikin gidan Afghanistan din Tariq Arian ya ce 3 daga cikin maharan sun hallaka yayin farmaki, tuni dai dakarun wanzan da zaman lafiya suka killace harabar makarantar domin tabbatar da cikakken tsaro.