1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Morsi na Masar ya yi rantsuwar kama aiki

Martin MunoJune 30, 2012

Sabon shugaban Masar zai ci gaba da shagulgulan kama aiki a jami'ar birnin Alkahira. Mohammed Morsi na kungiyar 'yan uwa musulmi ne shugaban farar hula na farko.

https://p.dw.com/p/15OeF
In this image made from Egyptian State Television, judges from Egypt's Supreme constitutional court applaud Mohammed Morsi, center, after he was sworn in as President in Cairo, Egypt, Saturday, June 30, 2012. Islamist Mohammed Morsi has been sworn in before Egypt's highest court as the country's first freely elected president, succeeding Hosni Mubarak who was ousted 16 months ago.(Foto:Egyptian State TV/AP/dapd)
Hoto: Reuters

Shugaban Masar Mohammed Morsi da ke zama na farko da aka zaba karkashin Jamhuriya ta biyu ya yi rantsuwar kama aiki dazu-dazunnan a gaban kotun tsarin mulkin kasar da ke birnin Alkahira. Shi ne dai shugaban farko da aka zaba karkashin inuwar jam'iyyar da ke da rajin addinin musulunci, wanda kuma ba shi da alaka da sojojin kasar.

Shugaba Morsi zai yi tattaki zuwa jami'ar birnin Alkahira domin ci gaba da gudanar da shagulgulan kama aiki, tare da gudanar da jawabi ga 'yan kasar domin bayyana manufofin gwamnatinsa. Babban kalubalen da ke gaban shugaban na Masar a halin yanzu shi ne na raba madafaun iko da majalisar mulkin sojoji, wadda Mubarak ya danka wa mulki bayan da guguwar neman sauyi ta yi awon gaba da kujerarsa ta mulki.

Tuni dai Morsi da aka zaba karkashin kungiyar 'yan uwa musulmi ya fara tattaunawa da bangarorin siyasa daban daban da nufin neman kafa gwamnatin hadaka da za ta fiskanci kalubale na tattalin arziki da kuma hadin kan kasa.

Mawallafi: Mouhamadou Awal
Edita: Saleh Umar Saleh