1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD: Saudiyya ta keta dokokin yaki a Yemen

Ramatu Garba Baba
October 4, 2017

A wannan Laraba Majalisar Dinkin Duniya ta sanya sunan Saudiyya da ke jagoranta yaki a kasar Yemen cikin kasashen da suka keta dokokin yaki ganin daruruwan yaran da suka mutu sanadiyyar hare-harenta.

https://p.dw.com/p/2lE8c
Jemen Frauen Engagement für Kriegsopfer
Hoto: DW/M. Alhadry

Saudiyya da ke taimaka wa gwamnatin Shugaba Abdourabuh Mansour Hadi don yakar 'yan tawayen Houthi ta sami kanta a cikin layin kasashen da suka taka dokokin yaki na duniya bisa rawar da kasar ta taka a rikicin kasar Yemen da ya lakume rayukan mutane fiye da dubu biyu a bara. Akalla 700 daga ciki wadannan alkaluman yara kanana ne inji rahoton Majalisar Dinkin Duniya, abin da ke nufin kashi 50 cikin 100 na yaran da suka hallaka a yakin Yemen a bara ya auku ne a sanadiyyar hare haren da dakarun kawance da Saudiyya ke jagoranta suka kaddamar a cikin kasar.

A daya bangaren kuwa Majalisar Dinkin Duniya ta ayyana kasar ta Yemen a matsayin kasar da ke cikin mawuyacin hali da tsananin bukatar taimako ganin mutane akalla miliyan bakwai ne ke fuskantar barazanar yunwa da kuma barkewar cutar amai da gudawa yanzu haka a kasar ta Yemen.