1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

MDD na fargabar rincabewar rikicin Yemen da Gabas ta Tsakiya

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
January 13, 2024

Amurka da kawayenta ne suka kaddamar da hare-hare da dama kan kasar, a kokarinsu na farwa 'yan tawayen Houthi

https://p.dw.com/p/4bD0V
Hoto: Mohammed Hamoud/Anadolu Agency via picture alliance

Majalisar Dinkin Duniya ta nuna damuwarta kan cewa rikicin da aka fara fuskanta a Yemen game da hare-haren jiragen ruwa a Kogin Baharmaliya, ka iya zama silar gaza kawo karshen rikicin kasar da aka jima ana fama.

Karin bayani:Bahar Maliya: Takaddamar Amurka da Houthi

Jakadan Majalisar Dinkin Duniya a Yemen Hans Grundberg ne ya yi wanna jawabi, yana mai cewar wajibi ne a kare fararen hular kasar Yemen, tare da kokarin yayyafawa wutar rikicin ruwa don samun dawwamammen zaman lafiya a yankin.

karin bayani:Iran na yunkurin kawo karshen yakin Yemen

A cikin makon nan da muke bankwana da shi ne dai Amurka da kwayenta suka kaddamar da hare-hare da dama kan kasar, a kokarinsu na farwa 'yan tawayen Houthi masu samun goyon bayan Iran, da ke ci gaba da kai hari kan jiragen ruwan da ke bi ta Baharmaliya, a matsayin martanin yakin da Isra'ila ke yi a Gaza.