1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Lafiya

Somaliya tana cikin matsanancin yunwa

Suleiman Babayo ATB
October 18, 2022

majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa yunwa tana ci gaba da ta'adi sakamakon farin mafi muni cikin shekaru 50 da ake fuskanta a kasar Somaliya.

https://p.dw.com/p/4IMSa
Afirka I Yunwa ta fadada a Somaliya
Yunwa ta fadada a SomaliyaHoto: Feisal Omar/REUTERS

Asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya, UNICEF, ya ce farin da ake fuskanta a kasar Somaliya ya kasance mafi muni ga kasar cikin shekaru 50 da suka gabata. A wannan Talata mai magana da yawun asusun, James Elder ya ce ana bukatar kimanin kudi Dalar Amirka milyan dubu-biyu saboda a tunkari matsalar.

Jami'an asusun na UNICEF ya kara da cewa a watan Agusta da ya gabata kadai kimanin yara 44,000 aka kwanatar a asibiti sakamakon matsananciyar yunwa. Kimanin mutane milyan-takwas kusan rabin mutanen kasar ta Somaliya farin ya shafa a cewar Majalisar Dinkin Duniya, dama kasar tana cikin tashe-tashen hankula na tsageru masu kaifin kishin addinin Islama.