1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Maslaha ga rikicin Sudan da Sudan Ta Kudu

April 3, 2013

Duk da ci gaban da aka samu a kokarin warware rikicin Sudan, da Sudan Ta Kudu, har yanzu da sauran rina a kaba.

https://p.dw.com/p/189Bv
[30994360] Heglig conflict epa03193946 Sudanese soldiers wave the Sudanese flag during their celebration in Heglig, Sudan, 23 April 2012. The European Union on 23 April urged Sudan and South Sudan to stop their escalating conflict, as France warned that the bloc might resort to sanctions to pressure the two sides into ceasing hostilities. They urged South Sudan to make good on promises to withdraw from the disputed Heglig oil fields and on Sudan to stop air raids on South Sudanese territory. EPA/STR
Hoto: picture-alliance/dpa

A wannan Alhamis (04.04.2013) ne wa'adin janye dakaru daga kan iyakar da kasashen Sudan da Sudan Ta Kudu ke takaddama akai ke cika, sakamakon yarjejeniyar da sassan biyu suka sanyawa hannu domin kawo karshen fito na fiton da suka yi a baya. Sai dai duk da cewar ba a kai ga warware rikicin da ke tsakanin su baki daya ba, amma an sami ci gaba.

Tunma gabannin Sudan Ta Kudu ta sami 'yanci a shekara ta 2011, dukkan sassan biyu na yin ja-in-ja game da rabon kudaden da suke samu daga kasuwancin man fetur. Sulusin rijiyoyin man din a wancan lokacin suna yankunan da a yanzu ke karkashin Sudan Ta Kudu ne, amma kuma bututun da ke safarar man fetur din ya ratsa ne ta Sudan Ta Arewa, amma bayan rikicin daya barke a tsakanin sassan biyu, Sudan Ta Kudu ta katse jigilar cikin watan Janairun shekara ta 2012, wanda kuma Andrew Natsios, tsohon jakadan Amirka a Sudan, ya shaidawa tashar DW cewar bangarorin biyu na bukatar juna domin ci gaban tattalin arzikinsu:

Ya ce "A lokacin da aka dakatar da jigilar man fetur a tsakanin Sudan da Sudan Ta Kudu, dukkan bangarorin biyu sun yi fama da matsalar tattalin arziki, kuma ko da shike suna da tarihin gaba da juna, amma idan ba su hada kai ba, to, kuwa dukkan gwamnatocin biyu da kuma al'ummomi daga sassan biyu za su fuskanci matsananciyar rayuwa."

A Sudanese engineer points at the damage to an oil pipeline in a largely damaged oilfield in Heglig April 23, 2012. Sudanese President Omar al-Bashir vowed on Monday not to negotiate with South Sudan after it occupied the oil-producing Heglig region. Weeks of border fighting have brought the neighbours closer to a full-blown war than at any time since the South split away from Sudan as an independent country in July. REUTERS/Mohamed Nureldin Abdallah (SUDAN - Tags: POLITICS CIVIL UNREST ENERGY BUSINESS)
Hoto: Reuters

Tasirin katse jigilar man fetur ga kasashen biyu

Dama dakatar jigilar ta janyo hauhawan farashin kayayyaki a Sudan Ta Arewa da fiye da kaso 28 cikin 100 a shekara ta 2012, yayin da tattalin arzikinta kuwa ya sami koma baya da fiye da kaso 11 cikin 100. Ita kuwa Sudan Ta Kudu, wadda ta dogara da man fetur wajen samun kudaden shigarta, na bukatar inganta rayuwar al'ummar ta ta hanyar samar da makarantu da asibitoci da kuma hanyoyi. Kai hatta ma da batun biyan albashi kamar yanda Andrew Natsios, tsohon jakadan Amirka a Sudan, ya shaidawa tashar DW:

Ya ce " A nazarin da na yi cikin littafin da na rubuta, akwai kimanin mutane dubu 400 da gwamnatin Sudan Ta Kudu ke biyansu albashi. dubu 100 ma'aikata ne, yayin da dubu 150 kuma ke zama sojoji, kana wasu dubu 150 ke zama mayakan sa kai da gwamnati ke kula da su, kuma take kiransu a duk lokacin da bukata ta taso, kuma hanyar hana barkewar rikici a Sudan Ta Kudu itace sanya kowa da kowa cikin jerin wadanda gwamnati ke biya."

(L-R) Pagan Amum, south Sudan chief negotiator, South Sudan's President Salva Kiir, former president of Nigeria Abdulsalam Abubakar, Chief African Union mediator Thabo Mbeki, former Burundi president Pierre Buyoya and President of Sudan Omar Hassan al-Bashir meet during talks in Ethiopia's capital Addis Ababa September 24, 2012. Leaders from Sudan and South Sudan will meet on Sunday for the first time in a year to try to agree on border security so that South Sudan can start exporting oil again, a lifeline for both economies. REUTERS/Tiksa Negeri (ETHIOPIA - Tags: BUSINESS COMMODITIES POLITICS)
Hoto: Reuters

Mafita ga rikicin dake tsakanin Sudan da Sudan Ta Kudu

Yarjejeniyar da sassan biyu suka kulla a cikin watan Maris dai ba ta warware daukacin batutuwan dake ingiza rikici a tsakanin su ba, musamman batun yankin Abyei - mai arzikin man fetur, da na cancantar zama dan kasa, harma da batun kan iyaka. Lamarin da Magdi el-Gizouli, jami'i a cibiyar nazarin tafkin Rift da ke yankin na Sudan, ya ce akwai jan aiki a gaban kasashen Sudan da Sudan Ta Kudu wajen shawo kan rikicin iyakar su:

Ya ce " Wannan iyakar da suke takaddama akanta, tana da tsawo sosai, kuma mai tsarkakiyar gaske, domin kuwa ba wai kawai wurin gudanar da ayyukan soji na kasashen biyu ba ne, harma wuri ne da 'ya tawaye da ma kungiyoyin mayakan sa kai daban daban ke cin karensu babu ba, wadanda kuma suka taba nuna goyon baya ga wani bagare a lokacin da suke yakar juna."

A yanzu dai shugaba al-Bashir ya sanar da kudirin kai ziyara zuwa Sudan Ta Kudu, yayin da ita kuwa Sudan Ta Kudun ke fatan samar da bututun da jigilar man ta kasashen Kenya da Djibouti a matsayin shirin ko ta kwana don kaucewa wani rikicin da ka iya barkewa a tsakanin su nan gaba.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Usman Shehu Usman