1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masar ta yi gyaran kundin tsarin mulki

March 20, 2007
https://p.dw.com/p/BuPE

Majalisar dokokin Masar ta amince da gyare gyare a wasu dokoki masu sarkakiya na kundin tsarin mulkin ƙasar, wanda yan adawa suka ce babbar koma baya ce ga dimokradiya a ƙasar ta gabas ta tsakiya. Shugaban ƙasar Hosni Mubarak ya gabatar da yin kwaskwarima ga kundin tsarin mulkin a wani mataki da ya ce na haɓaka tafarkin dimokradiya a ƙasar wadda ya shafe shekaru 25 yana shugabancin ta. A hannu guda yan adawa sun ce gyagyaren kundin tsarin mulkin ya yi tarnaki ga bangaren shariá na sa ido a kan zaɓe wanda suka ce hakan ne kawai zai kare yin maguɗin kuriú. Bugu da ƙari sabbin dokokin sun baiwa shugaban ƙasar ƙarin ƙarfin iko a kan harkokin tsaro. Kakakin ƙungiyar Muslim Brothers babbar jamíyar adawa a majalisar dokokin ta zargi gwamnatin da zartar da dokoki na kama karya.