1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mali za ta rufe kasuwannin dabbobi da ke karkashin Fulani

September 21, 2024

Gwamnatin kasar Mali ta ce za ta rufe kasuwannin sayar da shanu masu yawa a kasar musamman ma wadanda al'umar Fulani ke gudanar da su.

https://p.dw.com/p/4kviD
Hoto: Seyoum Getu/DW

Wannan mataki da hukumomin birnin birnin Bamako suka dauka, ya zo ne bayan wani hari mai muni da wata kungiya mai alaka da al-Qaeda ta kai a Malin a ranar Talata, harin kuma da ya haddasa asarar rayukan gomman sojoji.

Kungiyar ta'addan ta JNIM, ta dauki alhakin harin da aka kai a sansanin horar da jami'an soji a Bamakon da ma filin jirgin sama da ke wajen birnin.

Su dai Fulanin da galibin su makiyaya ne da ke rungume tsarin kiwon dabbobi na gargajiya na baje ne a kasashe da dama na yankin yammacin Afirka.

Kuma suna da adadi mai yawa a cikin mayakan tawaye da ke kai hare-hare a tsakiyar kasar Malin.

Gwamnan yankin Bamako Abdoulaye Coulibaly ya ce za a rufe kasuwannin shanun ne da bai ba da lokacin budewa ba, saboda dalilai masu nasaba da tabbatar da doka da oda.