1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Makomar tawagar masu sa ido a rikicin Siriya

February 12, 2012

Kungiyar Kasashen Larabawa ta shiga tunanin fadada tawagar masu sa ido a Siriya bayan murabus din shugabanta Mohamad Ahmed Moustapha al-Dabi

https://p.dw.com/p/142G0
epa03045015 An undated photograph taken from an image made available by Mustafa Mustafa al-Dabi shows Mustafa al-Dabi posing for a photograph in his military uniform, in Sudan. Al-dabi the mission's chief of Arab league delegation in Syria, said the mission was still in its early days and needed more time to assess the problems on the ground. He said 16 newly arrived observers were joining 50 colleagues on the ground. 'Give us more time and then criticize our work,' al-Dabi was quoted by Arab media as saying. He was severely criticized by Syrian opposition for saying he had seen 'nothing frightening' on his first visit to Homs, at the heart of the country's 10-month uprising. Syrian opposition also asked for the removal of al-Dabi who served in the Sudanese President Omar al-Bashir army who is under an International warrant regarding genocide in Dafur. EPA/STR BEST QUALITY AVAILABLE +++(c) dpa - Bildfunk+++
Mustafa al-Dabi shugaban tawagar masu sa ido a SiriyaHoto: picture-alliance/dpa

Shugaban tawagar da Kungiyar Kasashen Larabawa ta tura a Siriya, wato Mohamad Ahmed Moustapha al-Dabi ya yi mubabus.

Cemma dai Moustapha al-Dabi, na shan suka daga kasashen ketare dangane da rawar da suka ce ya taka, a ta'asar da ta wakana a yankin Darfur na kasar Sudan.

Albakarcin taron na yau, kungiyar kasashen larabawa, za ta tattanawa game da yiwuwar fadada tawagar sa ido kasar Siriya, ga sauran kasashen da ma na musulmi ba.Wata mai magana da yawun gwamnatin Siriya ,Bassma Kodmani ta ce gwamnati ta amince da hakan:Wannan na matsayin zabi ga aikin komitin Sulhu na Majalisar Dinkin, tawagar za ta iya taimakawa a kawo karshen yakin ta hanyar hawa tebrin shawara tsakanin bangarori biyu.

To saidai kamin a kai ga wannan mataki, ana ci gaba da gwabza fada tsakanin dakarun gwamnati da sojojin da suka suka burjine mata.

Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Abdullahi Tanko Bala