1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Makomar Somaliya bayan zaben shugaban kasa

Maja DreyerSeptember 10, 2012

kasashen duniya na fatan sabon shugaban Somaliya ya samar da zaman lafiya da ci gaba a kasar . Sai dai 'yan Somaliya da ke da zama a ketare na ganin cewar da kamar wuya a magance matsalar tsaro cikin kakkanin lokaci..

https://p.dw.com/p/1668C
A woman holds up election campaign posters of Somalia's President Sheikh Sharif Ahmed in Mogadishu, September 9, 2012. The presidential election will be held on September 10. REUTERS/Feisal Omar (SOMALIA - Tags: ELECTIONS POLITICS TPX IMAGES OF THE DAY)
Mata ma sun gudanar da yakin neman zabeHoto: Reuters

'Yan Somaliya ne dai ke saye da sayar da kayan lambu da sauran kayan bukatun yau da kullum a Unguwar Eastleigh da ke birnin Nairobin Kenya. Hasali ma dai ya na daya daga cikin wuraren da suka mamaye tun bayan da suka kaurace ma kasar ta Somaliya sakamakon yaki da ta ke fama da shi. Duk ma dai da Zaben 'yan majalisa da ma dai na shugaban kasa da aka gudanar, bai sa 'yan Somaliya da ke da zama a kenya sha'awar komawa kasarsu ta asali ba. Maimakon haka ma dai, hada guywa suke yi domin kafa kananan masana'antu ciki kuwa har da Hotel. Abubakar Sheikh Ali,  wanda daya ne daga cikin wadanda suka zuba hannu jari wajen gina hotel "Ben Ali" mai dakunan 114 a Nairobi ya ce al'amarin kafa masana'antu a  Mogadischo na ba su tsaro.

"Muna da wani katafaren hotel a Mogadischu, wanda sojojin kasar Habasha suka ragargaza lokacin yaki. Muna so mu sake gina shi. Amma muna ganin cewar bakin alkalami ya bushe saboda al'amura ba su daidaita a Mogadishu ba."

Somali President Sheikh Sharif Sheikh Ahmed arrives to mark the first year anniversary since the ouster of militant Al Shabaab fighters from the capital Mogadishu August 6, 2012. REUTERS/Omar Faruk (SOMALIA - Tags: CIVIL UNREST POLITICS ANNIVERSARY)
Sharif Sheikh Ahmed na daya daga cikin 'yan takaraHoto: Reuters

Baya ga Kenya dangin shi Ben Ali na neman kudi ne a kasashen Djibuti da Somaliland da Sudan ta kudu da  kuma Uganda. Sun juya ma kasarsu baya ne saboda hasarar kudi da ya kai miliyon  16 na dollar Amirka da suka yi  a inda baya ga hotel, suka asarar dukkanin kadarorin da suka mallaka a Mogadischu. Duk da cewa an zabi shugaban mai cikakken iko a wannan rana (10 ga watan satumba 2012). Amma dai Abubakar sheikh Ali ya ce wannan mataki bai zai zai inganta halin rayuwar talakawa ba matikar gwamnati ba ta farka daga barci ba.

"Zaman lafiya ba zai samu a Mogadischu ko ma dai Somaliya ba  sai idan mutane sun samu ayyukan yi maimakon dogaro da aikin sojan sa kai wajen samun kudin shiga. Wannan ya na nufin cewar akwai bukatar kafa masana'antu domin a samu guraben aiki. A halin yanzu kashi biyar ko 10% ke da aikin yi. Sauran kashi 95% na fama ne da zaman kashe wando. A wannan yanayi ba abin mamaki ba ne, matsalar tsaro ta ci gaba da zama karfen kafa."

Akasarin 'yan Somaliya da ke gudun hijira na danganta zaben 'yan majalisa da na shugaban kasa da ci gaban mai hakon rijiya. Shi ma Emmanuel Kisangani jami'i a cibiyar nazarin al'amuran tsaro da ke mazauninta Nairobin Kenya, ya ce  cin hanci da karbar rashawa na ci gaba da tasiri a yunkurin da ake yi na mayar da Somaliya kan kyakkyawar turba.

In a photograph taken Wednesday, Aug. 1, 2012 and released by the African Union-United Nations Information Support team Thursday Aug. 2., 2012. A man waves the Somali national flag ahead of the arrival of Somali President Sheik Sharif Sheik Ahmed (not seen) in Balad town, Somalia, in Middle Shabelle region approx. 40km north east of the capital Mogadishu. Balad was until recently, under the control of the Al-Qaeda-affliated terrorist group Al Shabaab until an offensive by the Somali National Army (SNA) supported by the African Union Mission in Somalia (AMISOM) forces on 26 June drove out the extremists, liberating the town and its people, and bringing the area under the control of the UN and internationally-backed Transitional Federal Government (TFG) whose mandate expires on 20 August. (AP Photo/AU-UN IST / Stuart Price).
Matsalar tsaro ba ta hana su yin alfahari da SomaliyaHoto: dapd

"Mambobin gwamnatin wucin gadi sun tsaya takara a matakai daban daban domin su ci gaba da kakkange madafun iko. Saboda haka wuka da nama na hannun jami'an gwamnati mai ci a yanzu. Alhali suna cikin manyan jami'an da aka zarga da cin hanci da kuma karbar rashawa."

Duk da yankar kauna da al'uma suka nuna musu, tsofoffin masu fada a ji na gwamnatin Somaliya sun yi amfani da dukiyarsu wajen samun mukami. Ko da a zaben kakakin majalisar dokokin na Somaliya da ma dai na shugaban kasa, sai da masu gida rana suka taka rawar gani.

Mawallafi: Mouhamadou Awal Balarabe
Edita: Yahouza sadissou Madobi