1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Makomar rikicin Siriya

February 24, 2012

Dakarun Siriya sun cigaba da murkushe masu zanga-zanga a yayin da gamayyar kasa da kasa ta kaddamar da taron neman matakan diplomasiyya

https://p.dw.com/p/149tC
Tunisia's Foreign Affairs Minister Rafik Abdessalem (C) addresses the Friends of Syria Conference in Tunis, February 24, 2012. Western and Arab nations meeting on Friday will demand that Syria implement an immediate ceasefire to allow aid in for desperate civilians in the absence of an international consensus on intervention to end a crackdown on an 11-month-old revolt. REUTERS/Jason Reed (TUNISIA - Tags: POLITICS)
Taron kungiyar tuntuba da sassanta rikicin SiriyaHoto: REUTERS

Shugabanin Larabawa a wannan juma'ar sun yi kira da a aika da wata tawagar masu wanzar da zaman lafiya zuwa Siriya, a wani taron da aka kaddamar da zuman matsawa gwamnatin Damascus da ta dakatar da zud da jinin da ke gudana, ta kuma bar ma'aikatan agaji su kai tallafi ga inda ake bida. Sakatariyar harkokin wajen Amurka Mrs Hillary Clinton, ta ce shugaba Basahr Al Assad zai fuskanci hukunci mai tsauri sakamakon rashin kulawa da kiraye-kirayen da alummar kasa da kasa ta yi ta masa na ya daina murkushe 'yan adawa. Haka nan kuma ministan harkokin wajen Faransa Alain Juppe, ya kwatanta majalisar 'yan adawan Siriyar ta SNC a matsayin halastacciyar gwamntin kasar.

Akalla mutane 22 suka hallaka ko bayan da kasashen larabawa da na yamma suka fara gudanar da taro a Tunisia, taron da suka yi wa take "taron kolin kawayen Siriya" wanda ke da burin aikawa gamnatin Assad da kakkarfar sako.

Wannan taro yana zuwa ne wuni biyu kafin a kira alummar Siriyar zuwa jefa kuri'a kan sabon kundin tsarin mulkin da zai kawo karshen mulkin jamiyyar Baath duk da cewa zai barwa shugaban kasa mafi yawan iko.

Mawallafiya: Pinado Abdu-Waba
Edita: Yahouza Sadissou Madobi