1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar dokokin Masar za ta zauna a wannan Talata

July 9, 2012

Shugaban ƙasar Masar Mohammad Mursi ya shure dokar rusa Majalisar Dokoki da sojoji su ka rattabawa hannu.

https://p.dw.com/p/15UOp
epa03264475 (FILE) A file photo dated 23 January 2012, shows the first Egyptian parliament session after the revolution that ousted former President Hosni Mubarak, in Cairo, Egypt. Media reports on 14 June 2012 state that the Supreme Constitutional Court ruled that one third of seats in parliament, allocated for independents, were void. The court described as unconstitutional an election law that allowed candidates from political parties to stand for independents' seats in the polls held late last year. It was not clear if the ruling means parliament would be dissolved. EPA/KHALED ELFIQI +++(c) dpa - Bildfunk+++
Ägypten Parlament KairoHoto: picture-alliance/dpa

Da ya ke wa manema labarai jawabi, kakakin majalisar ya ce za su zauna a goben da misalin karfe goma agogon GMT.

Majalisar dai ta ɗauki wannan matsayi ne bayan da sabon shugaban ƙasar Muhammad Mursi a jiya lahadi ya bada umarnin ta koma zaman ta, sai dai kuma sojojin ƙasar da ma dai kotun ƙolin kasar ba su amince da wannan matsayi da shugaban ƙasar ya ɗauka ba inda kotun ta ce za ta zauna a gobe (Talata) domin duba wannan mastayi da shugaban ƙasar ya ɗauka don sanin tudun dafawa.

Masu sanya idanu kan siyasar kasar ta Masar dai na ganin wannan lamari ka iya jefa jaririyar gwamnatin Mursi cikin rikici da rundunar sojan ƙasar da ma dai ɓangaren shari'a.

Tuni dai wasu jam'iyyu ciki har da jam'iyyar Egyptian Social Democratic Party wadda ke da wakilai a majalisar su ka fara yin tur da wannan matsayi na shugaba Mursi da kakakin majalisar dokokin ƙasar inda su ka ce hakan karen tsaye ne ga ɓangaren shari'a to sai dai jam'iyyar 'yanuwa Musulmi ta Shugaba Mursi ta ce sam ba karen tsaye ta dau aniyar yi ga ɓanaren na shari'a ba.

Mawallafi : Ahmed Salisu
Edita : Yahouza Sadissou Madobi