1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD ta tattauna kan rikicin Isra'ila

May 12, 2021

Kwamittin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya bai cimma matsayar fitar da sanarwa ta hadin gwiwa ba a taron gaggawa da ya gudanar kan rikicin Isra'ila da Falasdinawa.

https://p.dw.com/p/3tJt5
Weltspiegel 12.05.2021 | Israel Konflikt | Gaza (Stadt)
Hoto: Mahmud Hams/AFP/Getty Images

Rashin cimma matsayar dai na zuwa ne bayan da Amirka da ke zama babbar kawar Isra'ilar ta nuna adawar hakan.

Amirka ta ce bata ganin cewa fitar da sanarwa zata iya yayyafa ruwa a wutar rikicin, sai dai kuma wakilai 14 cikin 15 na kwamittin sun yi amanar cewa sanarwar hadin gwiwa ka iya sassauta tashin hankali da ake ciki. Wakilin yankin gabas ta tsakiya na Majalisar Tor Wennesland ya yi gargadin cewa ta la'akari da yadda rikicin ke kara rincabewa, akwai fargabar rikicin ka iya sauya salo.

Ana dai ci gaba da lugudan wuta tsakanin bangarorin biyu, inda gomman mutane suka rasa rayukansu ciki har da yara a Gaza yayinda ita Isra'ila ta rasa wasu dakarunta.