1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Komi ya daidaita a Amirka

January 7, 2021

Hadin gwuiwar majalisar dokokin Amirka ya ci gaba da zaman shi, bayan da magoya bayan Donald Trump suka afkawa ginin majalisar kasar.

https://p.dw.com/p/3ncMA

Majalisar Dinkin Duniya gami da kasashe masu fada a ji a fadin duniya da suka hada da China da Jamus, sun bayyana abin da ya faru na afkawa harabar majalisar dokokin Amirka da wasu magoya bayan shugaba Donald Trump suka yi a matsayin karan tsaye ga demokaradiyya.

A kalla mutane hudu ne suka rasa rayukkansu cikinsu har da wata mata, inda kuma 'yan sanda suka chafke masu zanga-zanga sama da hamsin a arangamar da suka yi.

Kawo yanzu abubuwa sun fara daidaita a majalisar, kuma gaba kadan za a cigaba da shirin na tabbatarwa zababben shugaban kasar Joe Biden nasararsa.