1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Tanzaniya na jimamin mutuwar shugabanta

March 18, 2021

Jama'a a ciki da wajen Tanzaniya na ci gaba da aike wa da sakon ta'aziyya bisa mutuwar Shugaban kasar John Magufuli.

https://p.dw.com/p/3qmsS
Tansania President John Pombe Magufuli of Tanzania at State House in Dar es Salaam. Left is her vice president, Samia Suluhu Hassan.
Hoto: DW/Said Khamis

A yammacin Larabar nan ce dai Mataimakiyar Shugabar kasar Samia Suluhu Hassan ta sanar da cewa Shugaba Magufuli ya rasu a birnin Dar es Salaam. Sai dai sabanin cutar corona da ake ta rade-radin cewa ita ce ta kama shi da ba a ganinsa a bainar jama'a a 'yan kwanakin nan, mataimakiyar shugaban kasar ta ce Magufuli ya mutu a sakamakon wani nau'i na ciwon zuciya wanda ya kwashe shekaru fiye da 10 yana fama da shi.

A bisa tsarin mulkin Tanzaniya dai yanzu mataimakiyar shugaban kasa Samia Suluhu Hassan ce za ta maye gurbin Shugaba Magufuli, kuma za ta ja ragamar kasar har zuwa shekara ta 2025 lokacin da za a gudanar da sabon zabe.