1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ma'amala tsakanin Jamus da Indonisiya

July 10, 2012

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta gana da hukumomin Indonisiya a yunƙurin ƙarfafa dangataka tsakanin ƙasashen biyu.

https://p.dw.com/p/15Uzd
Indonesian President Susilo Bambang Yudhoyono, right, gestures during a joint press conference with German Chancellor Angela Merkel, left, after their meeting at Merdeka Palace, Indonesia, Tuesday, July 10, 2012.(Foto:Achmad Ibrahim/AP/dapd).
Angela Merkel da Susilo Bambang YudhoyonoHoto: dapd

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta gana da shugaba Susilo Bambang Yudho-Yono na Indonisiya a birnin Jakarta inda ta yadda zango.Ziyara wace ita ce ta farko da Merkel ke yi a yankin kudanci Asiya ,a ƙasar da ita ce, ta huɗu mafi yawan al'umma a duniya na zaman wata kafa ta ƙara ƙarfafa hulɗa tsakanin ƙasahen biyu.

A ganawar, shugabannin biyu, sun tattauna batutuwa da dama a ciki harda matsalar kuɗin da ake fuskanta a nahiyar Turai.Da ta ke magana da manema labarai, Merkel ta ce Indonesiya ta fahimci abin da ke faruwa a turai:

Ta ce Indonisiya ta gane halin da ake ciki, domin ita kanta a shekarun baya baya nan, ta yi fama da wahaloli, amma mu dukanin biyu mun yi imanin cewar abune dake wucewa.

Mawallafi: Abdourahman Hassane
Edita:Yahouza Sadissou Madobi