1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An gano Uranium din da ya bata a Libiya

March 16, 2023

Hukumomin kasar Libiya sun ce an yi nasarar gano makamashin Uranium tan 2.5 da hukumar kula da makamashin Nukiliya ta duniya IAEA ta sanar da bacewarsu.

https://p.dw.com/p/4OoGL
Libiya | Uranium | Makamashi
Nasarar gano makamashin uranium a LibiyaHoto: Israel Defense Force/U.S. military Central Command/AP/picture alliance

Kakakin rundunar sojoji masu biyayya ga Khalifa Haftar janar Khaled al-Mahjoub ne ya sanar da gano da Uranium din a tazarar kilomita biyar daga tashar da ake ajiye da su a Kudancin kasar.

Gabanin sanar da batan kwantinan daraktan hukumar ta IAEA Rafael Grossi ya bayyana abin a matsayin babban abin damuwa da ka iya haifar da matsalolin tsaro na nukiliya a kasar da yaki ya daidaita.

A shekarar 2003 ne dai tsohon shugaban kasar Libiya Mouammar Kadhafi ya amince da yin watsi da shirin kera makaman nukiliya, wanda a karkashin shirin ya amince wa masu binciken makamai shiga kasar kafin daga bisani guguwar sauyi ta hambarar da shi a shekarar 2011.