Lawyoyi a Niger sun fara wani yajin aiki
January 11, 2016Talla
Majalisar lawyoyin ta dauki wannan matakin ne don nuna bakin cikin kan kame-kamen da ake yi ma wasu 'yan siyasar adawar kasar da ake tuhumar da hannu a yunkurin kifar da mulkin da bai ci nasara ba.
Shugaban majalisar lawyoyin Samna Soumana Daouda ya ce ya na da kyau a gurfanar da wadanda ake zargi a gaban kotu ba wai a ci gaba da tsaresu ba.
Yanzu haka dai al'amura na ci gaba da zafafa a yayin da ake tsare da Hama Amadou dan takarar shugabancin kasar da katun kundun tsarin mulki ta amince da takararsa.