1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Lardin Kosovo ba zai rabu gida biyu ba

August 12, 2007
https://p.dw.com/p/BuEB

Bayan shawarwarin da suka yi baya-bayan nan, bangarorin 3 da ake yiwa lakabi da Troika wadanda ke tattaunawa dangane da makomar lardin Kosovo sun ce lardin ba zai rabu gida biyu ba zuwa yankin Albaniyawa da Sabiyawa ba. A shirye bangarorin da suka hada da wakilan KTT da Amirka da kuma Rasha su ke, su aiwatar da kowace yarjejeniya da za´a cimma tsakanin Sabiya da Kosovo, inji Wolfgang Ischinger wakilin kungiyar EU a tattaunawar.

Ischinger:

“Wani jan aiki ke gaban mu, amma bayan tattaunawar da muka da farko a birnin Belgrade da wadda muka yi jiya da yau a Pristina, mun gano cewa sassan biyu sun yi maraba da mu kuma dukkan su biyu sun tabbatar mana da cewa a shirye suke su ba mu hadin kai.”