1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Salon rayuwa

Labaran karya na yaduwa a Afirka

Mouhamadou Awal Balarabe
January 2, 2020

Kasashen Afirka da dama sun yin kaurin suna a fuskar yada labaran kanzon kurege da nufin cimma buri na kashin kai. Kafofin sada zumunta na zamani sun taimaka wajen yada labaran karya a Kamaru da Ghana da Afirka ta Kudu.

https://p.dw.com/p/3VbEW
Social Media-Nutzung in Afrika
Hoto: AFP/Getty Images/I. Sanogo

Yanzu haka dai ya zama al'ada a kasar Kamaru a kowanne mako a sami bullar sabon labarin bogi, wanda kuma sai bayan ya dauki hankalin al'umma kafin a san cewar ba sahihin labari ba ne. Al'umma sun dora alhakin bazuwar irin wadannan labaru a kan shafukan sadarwar na zamani.

A Afirka ta Ludu ma, labaran bogi sun zama gama gari a 2019 saboda kafofin sada zumunta na zamani sun zama hanya mafi sauki na samun labarai cikin sauki, ko da yake su ne jigon yada labaran karya.

Batun yada jita-jita ya dade yana wakana a kasar a kasar Ghana. Amma  jama'a na cewa zuwan shafukan intanet ya habbaka wannan dabi'a, inda yanzu bambance labarin gaskiya da na karya ke zama jidali ga 'yan kasar.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Rahotanni da Sharhuna

Rahotanni da Sharhuna