1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar Amnesty ta zargi hukumomin kasar Turkiya

Salissou BoukariApril 1, 2016

A wata sanarwa da ta fitar a wannan Jumma'a kungiyar Amnesty International ta ce hukumomin Turkiya sun mayar da 'yan gudun hijira da dama zuwa inda ake yaki a Siriya.

https://p.dw.com/p/1IO76
Amnesty International PK zur Lage der Menschenrechte 2015/2016 Selmin Çaliskan
Hoto: picture-alliance/dpa/P. Zinken

Kungiyar ta zargi hukumomin na turkiya ne da laifin maida 'yan gudun hijira da karfi da yaji ya zuwa kasar Siriya bayan da suka guje wa yake-yaken kasar ta Siriya. Cikin wata sanarwa ce dai da ta fitar a wannan Jumma'a kungiyar ta mai fafutukar kare hakin dan Adam ta ce ta samu labari ne daga shaidu da abubuwan suka faru a kansu kamar yadda Jean-François Dubost, shugaban sashen kula da kariyar al'umma a kungiyar ta Amnesty reshen kasar Faransa ya yi tsokaci:

"Mun je kasar Turkiya ba da dadewa ba, kuma mun je yankunan iyakokin kasar da Siriya, sannan mun tattara bayannai daga iyalai da dama da suka tabbatar an mayar da su zuwa kasar ta Siriya bayan da suka iso Turkiya kuma bayan da jami'an tsaro suka bincike su."

Hakan dai na zuwa ne kwanaki kalilan kafin sake mayar da gungun farko na 'yan gudun hijira da aka kora daga Turai zuwa kasar ta Turkiya kamar yadda yarjejeniyar da aka amince da ta ranar 20 ga watan jiya na Maris.