1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabon gwajin makamai a Koriya ta Arewa

Zulaiha Abubakar
July 25, 2019

Kasar Koriya ta Arewa ta harba wasu makamai masu cin takaitaccen zango har guda biyu cikin tekun Japan da ke yankin gabashin kasar kamar yadda gamayyar mataimakan gwamnatin kasar ta tabbatar.

https://p.dw.com/p/3Mh90
Nordkorea Kim Jong Un in Pjöngjang
Hoto: picture-allianvce/AP Photo/Korean Central News Agency

 Wannan gwaji na Koriya ta Arewa na zuwa ne yayin da kasar da Amirka ke fatan ci gaba da tattauna batun makaman nukila. Ministan tsaron kasar Japan Takeshi Iwaya ya bayyana takaicinsa game da faruwar wannan al'amari wanda ya kira da cin fuskar tanadin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya.

Babban jami'in ya jaddada aniyar kasar Japan hadin gwiwa da Koriya ta Kudu a aikin sanya ido da tattara bayanai domin mika wa gwamnatin Amirka gabanin ci gaban tattauna batun makaman nukular Koriya ta Arewa. Ko cikin watan Mayun sai da Koriya ta Arewa ta kaddamar da wani gwajin makamai mai razanarwa.