1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fafutukar cimma daidaito a Libiya

Abdourahamane Hassane
January 22, 2021

Wakilai na 'yan majalisun dokoki na Libiya na bangarori biyu da ke rikici kan iko sun soma yin wani sabon zagaye na tattaunawa a Maroko domin samun daidaito tsakanin sasan biyu.

https://p.dw.com/p/3oJHC
Marokko Rabat | Libyen Dialog
Hoto: AFP/F. Senna

Taron wanda ake yi Bouznika a kudancin Maroko ya hada 'yan majalisun dokokin na Tabruk wanda ke a karkashin ikon janar Haftar  da kuma wandanda ke yin biyaya ga gwamnatin wucin gadi da ke samun goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya. Kasar Libiya ta fada cikin wani hali na rishin tsayayyar gwamnati tun bayan faduwar gwamnatin Muammar Kadhafi a shekara ta 2011.