1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Karin watannin shida kafin rufe sansanin Dadaab

Salissou Boukari
November 16, 2016

Gwamnatin kasar Kenya ta sanar da dage batun rufe sansanin 'yan gudun hijirar kasar na Dadaab wanda ke a matsayin sansani mafi girma a duniya, da a baya ta kudiri aniyar rufewa a karshen wannan wata na Nuwamba.

https://p.dw.com/p/2SmZR
Flüchtlingslager Dadaab Kenia
Hoto: AP

Ministan cikin gidan kasar Kenyan Joseph Nkaissery ne ya bayyana hakan, abin da ya biyo bayan bukatar da hukumar kula da 'yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya UN HCR ta shigar a kan wannan batu domin ganin an jinkirta rufe sansanin na Dadaab, sannan kuma ministan ya ce mayar da 'yan gudun hijirar kasashensu, zai wakana ne cikin mutunci da girmamawa nan da watanni shida masu zuwa a sabon wa'adin da gwamnatin ta dauka na kammala ayyukan rufe wannan babban sansani.

Sansanin na Dadaab da ke kusa da iyakar kasar ta Kenya da Somaliya, na dauke  ne da 'yan gudun hijira akalla 280.000 wadanda akasarinsu 'yan kasar Somaliya ne da suka gudo tun daga shekara ta 1991, lokacin barkewar yakin basasa da kashe-kashen da masu kishin adini ke yi da kuma matsalar farin da suka tsinci kansu a ciki.