1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kara dagulewar al'amura a Siriya

March 26, 2012

Turkiya ta rufe ofishin jakadancinta a Damascus babban birnin Siriya

https://p.dw.com/p/14SJQ
In this photo released by the Syrian official news agency SANA, Syrian army soldiers and security officers inspect the blast area in front of a damaged building of the air intelligence forces, which was attacked by one of two explosions, in Damascus, Syria, on Saturday, March 17, 2012. Two "terrorist explosions" struck security targets in the Syrian capital Saturday morning, killing a number of civilians and security forces, the country's state news agency said. The report said preliminary reports indicated they blasts were caused by car bombs that hit the aviation intelligence department and the criminal security department. (Foto:SANA/AP/dapd)
Hoto: SANA

A sakamakon kara dagulewar halin tsaro a Siriya ma'aikatar harkokin wajen Turkiya ta sanar da rufe ofishin jakadancinta a Damaskus babban birnin kasar ta Siriya. Tun a makon da ya gabata ne dai ma'aikatar ta yi kira ga 'ya'yan Turkiya da ke zaune a Siriya da su gaggauta ficewa daga cikinta. Kenan Turkiya ta bi sahun kasashe da dama na Kungiyar Tarayyar Turai da Amirka da kasashen Gulf guda shida wadanda tuni suka dauki wannan mataki. Tun wasu makonni kenan dakarun gwamnatin Siriya ke kai wa 'yan adawa hari. A cewar Majalisar Dinkin Duniya mutane sama da dubu 8 ne suka rasa rayukansu a rikicin na Siriya ya zuwa yanzu.

Mawallafiya: Halima Balaraba Abbas
Edita: Mohammad Nasiru Awal