1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kanada za a tusa keyar jami'an diflomasiyya 41 na Indiya

Abdourahamane Hassane
October 20, 2023

Kasar Kanada ta ce za a tusa keyar jami'an diflomasiyya 41 na indiya zuwa kasarsu, sakamakon rikicin da ya barke tsakanin Ottawa da New Delhi.

https://p.dw.com/p/4XpoH
Indien Amritsar | Sikh-Proteste vor Goldenem Tempel
Hoto: REUTERS

Rikicin ya  biyo bayan kisan da aka yi a watan Yunin da ya gabata na wani shugaban 'yan awaren Sikh a kasar Canada. Hardeep Singh Nijjar, wanda aka kashe a kusan yammacin birnin Vancouver , dan gwagwarmaya  ne mai fafutukar kafa Khalistan, yankin Sikh mai cin gashin kansa a arewacin Indiya.Tun farko a cikin watan satumba da ya  gabata firaministan Kanada Justin Trudeau ya ce jami'an leken asirin Indiya na da hannu cikin wannan kisan, wanda ya haifar da rikicin diflomasiyya tsakanin Kanada da Indiya, sai dai Indiyar ta musunta zargin.