1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Jamus za ta bai wa Labanan kudaden karfafa tsaro

January 10, 2024

Yayin da rikici ke kara ta'azzara a kudancin Labanan, inda 'yan tawayen Hezbollah ke kai hare-hare a kan Isra'ila, Jamus ta ware wasu miliyoyin Euro domin amfanin Labanan.

https://p.dw.com/p/4b5pt
Ministar harkokin wajen Jamus, Annalena Baerbock
Ministar harkokin wajen Jamus, Annalena Baerbock Hoto: Michael Kappeler/dpa/picture alliance

Jamus za ta bai wa Labaran Euro miliyan 15, da za a yi amfani da su domin bai wa sojoji damar inganta tsaro a kudancin kasar, daidai lokacin da rikici ke kara ta'azzara tsakanin Isra'ila da 'yan tawayen Hezbollah.

A jawabin da ta yi a Beirut babban birnin kasar Labanan a wannan Laraba, ministar harkokin wajen Jamus, Annalena Baerbock ta ce gwargwadon taimakon da dakarun wucin gadi na Majalisar Dinkin Duniya suka samu a Labanan, gwargwadon su ma na kasar za su samu.

Minista Baerbock wadda ta bukaci da a dakatar da kai wa juna hare-hare a iyakar Labanan da Isra'ila, ta yi kiran kwance damarar yaki a tsakanin bangarorin duka biyu.

Cikin kalamanta dai ta ce bai kamata yaki da Isra'ila ke yi kan kungiyar Hamas a Gaza, ya zamo hujjar kunna sabuwar wuta ta rikici a yankin ba.