1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Jamus ya kammala ziyarar aiki a Afirka

Ramatu Garba Baba MNA
November 21, 2018

Shugaba Frank-Walter Steinmeier, ya nemi hadin kai a tsakanin kasashen Turai da Afirka a ziyarar farko da wani shugaban kasar zai kai a kasar Afirka ta Kudu a cikin shekaru 20.

https://p.dw.com/p/38gm1
Bundespräsident Steinmeier in Südafrika
Hoto: picture-alliance/dpa/B. von Jutrczenka

Shugaban ya tabo batutuwa da suka kunshi yaki da cutar HIV da matsalar fari da sauyin yanayi ke haifarawa. Wannan ziyarar wani tubali ne na ingantuwar dangantaka tsakanin kasashen biyu.

Daga shekara ta 2019 Afirka ta Kudun da Jamus za su cigaba da zama membobi a kwamitin sulhu na MDD, dangane da haka ne Steinmeier ya bayyana alakar kasashen biyu a matsayin abu mafi dacewa.Baya ga Afirka ta Kudu, Steinmeier ya ziyarci kasar Botswana.