1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Turkiyya na shan matsi kan Tekun Bahar Rum

Abdul-raheem Hassan
November 19, 2020

Ministan harkokin wajen Jamus Heiko Maas ya ce akwai yuwar kungiyar tarayyar Turai ta sake kakabawa gwamnatin Ankara takunkumi, idan ba ta jdena haddasa rikici a gabashin Tekun Bahar Rum ba.

https://p.dw.com/p/3lYOp
Coronavirus I Außenminister Heiko Maas
Hoto: Thanassis Stavrakis/AP/dpa/picture-alliance

Gwamnatin Jamus ta gargadin Turkiyya ta rage haddasa rikici a gabashin Tekun Bahar Rum in dai tana son tsira daga sabbin takunkumin kungiyar Tarayyar EU.

Da ya ke magana gabannin taron EU a watan Disamba, ministan harkokin wajen Jamus Heiko Maas ya ce dabara ta rage wa Shugaba Raccep Tayyip Erdgang na daukar mataki domin kaucewa abin zai biyo baya, Maas ya ce ziyarar Erdogan a gabashin Cyprus alama ce ta nuna tirjiya.