1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus za ta bunkasa tattalin arzikinta

June 2, 2020

A wani yunkuri na daidaita tattalin arzikin kasar, ministocin gwamnatin Jamus za su gudanar da taro da nufin kawo karshen kiki-kaka dangane da tallafin da gwamnatin kasar ta ware domin tallafawa masana'antun kasar.

https://p.dw.com/p/3d9AX
Angela Markel in Berlin 22.10.2014 Symbolbild USA Deutschland Beziehungen
Hoto: Getty Images/AFP/Odd Andersen

Biyo bayan ta'annatin da annobar Corona ta yi wa tattalin arzikin kasashe a fadin duniya, Jamus ta lashi takobin farfado da tattalin arzikinta.

Babban batun da ake gani ka iya mamaye tattaunawar da ministocin kasar suka shirya shi ne batun kamfanonin kera motoci da ke kan gaba wajen bai wa al'umma aiki a kasar, wanda mai magana da yawun jam'iyyar SPD ya ce zai yi matukar wuya a samu matsaya a wannan ranar.

Takaddamar da ta barke tsakanin bangaren jam'iyyar masu ra'ayin mazan jiya ta Angela Markel da ke da ra'ayin rage haraji da kuma sassautawa 'yan kasuwa da kuma jam'iyyar 'yan gaba dai-gaba dai ta SPD da ke ganin a damkawa kowa tallafinsa a hannunsa shi ne mafi a'ala.