1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jami'an Amirka sun sauka Turkiyya

October 17, 2019

A kokarin yayyafa wa rikicin arewacin Siriya ruwan sanyi, manyan jami'an Amirka da ke ke kokarin shiga tsakani sun isa Turkiyya domin tattauanawa da Shugaba Racep Tayyip Erdogan.

https://p.dw.com/p/3RRqS
Mike Pence und Mike Pompeo
Hoto: picture-alliance/AP Photo/J. Martin

Mataimakin shugaban kasar Amirka Mike Pence da sakataren harkokin wajen kasar Mike Pompeo, sun isa Ankara babban birnin kasar Turkiyyar, domin tattaunawa kan batun neman tsagaita buda wuta a yankin arewa maso gabashin Siriya.

Manyan jami'an biyu dai za su gana ne da Shugaba Racep Tayyip Erdogan a kan batun da shugaban na Turkiyya ya yi ta yin biris a kai.

Hasali ma bayyana rashin damuwarsa Mr Erdogan din ya yi da barazanar kakaba wa kasarsa takunkuman tattalin arziki da musamman kasar Amirka ta yi.

Mike Pence, wanda ke shiga Turkiyya a karon farko a matsayinsa na mataimakin shugaban Amirka, ya sauka Turkiyyar ne 'yan sa'o'i bayan nesanta kansa da Shugaba Donald Trump daga rikicin Turkiyya da Kurdawan arewacin na Siriya.

A kalaman nasa dai, Shugaba Trump, ya ce babu ta yadda hakan ya shafi Amirka.