1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jagoran 'yan awaren kamaru gaban kotu

Gazali Abdou Tasawa
November 1, 2018

Jagoran 'yan awaren yankin da ke amfani da Turancin Ingilishin kasar Kamaru Sisiku Julius Ayuk Tabe, ya bayyana a gaban kotun babban birnin kasar a wannan Alhamis domin neman beli.

https://p.dw.com/p/37XAT
Kamerun - Proteste
Hoto: Getty Images/AFP/Stringer

Jagoran 'yan awaren yankin da ke amfani da Turancin Ingilishin kasar Kamaru Sisiku Julius Ayuk Tabe wanda mahukuntan Najeriya suka kama a watan Janerun da ya gabata suka mika wa mahukuntan Kamaru ya bayyana a karon farko tun bayan kamunsa a wannan Alhamis a gaban kotun a birnin Yaounde shi da wasu 'yan awaren su tara. 

Jagoran 'yan awaren kasar ta Kamaru ya bayyana ne a gaban kotun domin sanin makomarsa  a game da bukatar neman belinsa da lauyoyinsa suka shigar a gaban kotun. 

Watanni 10 kenan dai rabo da a ga jagoran 'yan awaren yankin Ambazoniyar kasar ta Kamaru mai shekaru 46 a bainal jama'a ba, lamarin da ya jefa danginsa cikin fargabar makomarsa a hannun mahukuntan kasar ta Kamaru. Daga karshen zaman na yau dai kotun birnin na Yaounde ta tsaida ranar 15 ga watan Nowamba domin bayyana matsayinta a game da bukatar belin nasa.