SiyasaGabas ta Tsakiya
Siriya: Isra'ila na ci gaba da mamaye Golan
February 14, 2025Talla
Kungiyar Kare Hakkin dan Adam da ke sanya idanu a yakin Siriya ce ta sanar da hakan, inda ta ce ta samu rahoton an hango sojojin Isra'ila a birnin Al-Rafid kwanaki biyu bayan wasu rahotanni sun ce an hango sojojin Isra'ilan sun shiga birnin Kudana. Kungiyar ta ce an hango motocin sojojin Isra'ilan ma har guda 12 a birnin Saidna al-Golan, inda sojojin suka kafa wajen binciken ababen hawa. Sai dai rundunar sojojin Isra'ilan ta ce, ba za ta ce komai a kai ba.