1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hari kan gangamin siyasa a Pakistan

Lateefa Mustapha Ja'afar
July 13, 2018

Kungiyar 'yan ta'addan IS ta dauki nauyin harin da aka kai kan wani gangamin siyasa a kasar Pakistan da ya hallaka mutane da dama.

https://p.dw.com/p/31Qd3
Pakistan Selbsmordanschläge
Hari yayin gangamin siyasa a PakistanHoto: picture-alliance/Xinhua/Irfan

Kamfanin dillancin labarai na Amaq da ke yada farfagandar kungiyar, ya bayyana cewa IS din ce ke da alhakin kai harin na kunar bakin wake da aka kai a garin Mastung da ke gundumar Balochistan da ya hallaka mutane sama da 80. Harin wanda ke zaman mafi muni da aka kai kan gangamin siyasa a baya-bayan nan a Pakistan din, na zuwa ne gabanin babban zaben kasar da za a gudanar a ranar 25 ga wannan wata na Yuli da muke ciki.