1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iraki: Bam ya kashe mutane a bikin Aure

Abdul-raheem Hassan
March 9, 2017

Hukumomi a kasar Iraki na cewa 'yan kunar bakin wake sun hallaka mutane 21 a lokacin da suke shagulgulan jajiberen bikin Aure a yankin Al-Hajaj da ke arewacin birnin Tikrit.

https://p.dw.com/p/2YtSd
Irak Bagdad Bomben Anschlag
Hoto: Reuters

Likitoci da ke karban jinya sun ce akwai mutane 25 da ke fama da munanan raunuka, sai dai kawo yanzu babu wadanda suka dau alhakin kai harin, amma hukomi a kasar sun ce kungiyar IS ta sha kai hare-hare makamancin wannan a kan fararen hula da ma jami'an tsaro.

A yanzu dai dakarun gwamnatin Iraki na fafatawa a yammacin birnin Mosul na ganin sun karbe iko na sauran yankunan da ke karkashin ikon kungiyar ta IS, inda wasu rahotanni ke cewa tuni jagoran kungiyar Abu Bakr al-Baghdadi ya tsere daga birnin.