1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hillary Clinton ta baiyana buƙatar Amurika ta ƙarfafa ma'amala da Najeriya.

August 9, 2012

Ziyarar Sakatariyar harkokin wajen Amurika a wasu ƙasashen Afirka ta haddasa mahawara game da hammaya tsakanin Amurika da China wajen samun angizo a ƙasashen nahiyar.

https://p.dw.com/p/15n4W
US Secretary of State Hillary Rodham Clinton waves as she arrives for a meeting of the Action Group for Syria at the European headquarters of the United Nations, UN, in Geneva, Switzerland, Saturday, June 30, 2012. The United States and Russia failed on Friday to bridge differences over a plan to ease Syrian President Bashar Assad out of power, end violence and create a new government, setting the stage for the potential collapse of a key multinational conference that was to have endorsed the proposal. (Foto:Keystone, Laurent Gillieron/AP/dapd)
Hoto: AP

A cigaba da rangadin aikin kwanaki 11 dfa ta kai a Afirka, Sakatariyar harkokin wajen Amurika Hillary Clinton ta gana a wannan Alhamis da hukumomin Naeriya.

Masu sharhi game da Afrika, na fasara rangadin na Clinton a Afirka a wani yunƙurin Amurika na ƙara samun angizo a nahiyar, a daidai lokacin da ƙasar China ke ƙara samu gindin zama.

A duk ƙasashen Afrika da Hillary Clinton ta ziyarta ta tattana da magabatan game da batutuwa masu mahimmanci, wanda suka jiɓanci kare 'yancin bani Adama, demokraɗiyya da kuma ma'amala tsakanin Amurika da wannan ƙasashe, tare da yin hannunka mai sanda ga shugabanin ƙasashen dangane da ma'amalarsu da China.

Ita dai ƙasar ta China saɓanin Amurika,ta na bada tallafi da ƙasashen Afrika ba tare da yin la'akari ba da batutuwan da suka shafi demokraɗiya ko kuma kare 'yancin bil Adama.

A tsukin shekaru goma da suka gabata, ƙasar China ta samu karɓuwa matuƙa a Afrika, al'amarin da ya fara dusashe angizon ƙasashen Turai da Amurika.

epa03046191 (FILE) A file photograph Goodluck Ebele Jonathan, President and Commander-in-Chief of the Armed Forces of the Federal Republic of Nigeria speaks during the general debate at the 66th session of the United Nations General Assembly at United Nations headquarters in New York, New York, USA, on 21 September 2011. Media reports state on 31 December 2011 that President Goodluck Jonathan has declared a state of emergency in areas affected by attacks from the Islamist group Boko Haram. Borders will be temporarily closed in the north-eastern states of Yobe and Borno, and central state of Plateau. EPA/JASON SZENES *** Local Caption *** 00000402928322 +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture-alliance/dpa

Jakkie Cilliers manazarci ne a cibiyar tsaro dake birnin Pretoriya na Afrika ta Kudu, ya bada dalilan hammayar mai tsanani tsakanin China da Amurika a nahiyar Afrika:

" Hammaya tsakanin Amurika da China a nahiyar Afrika ta ƙarfafa domin ko wace ƙasa daga cikinsu na buƙatar ƙulla dangatakar kasuwanci.Yanzu Afrika ta daina zama 'yar amshin shata a fagen siyasa da kasuwanci na duniya , ta rikiɗa zuwa wata babbar kasuwar duniya, wadda kowa ke buƙatar samun abokan hulɗa."

China tare da haɗin gwiwa da ƙasashen Brazil, Rasha, Indiya da Afrika ta Kudu sun kafa wata ƙungiyar ƙasashe masu tashe ta fannin bunƙasar tattalin arziki da suka raɗawa suna BRICS.

Manahajojin wannan ƙungiya sun sha bambam da tsarin da aka sani irin na turawan mulkin mallaka da Amurika game da ma'amala tsakanin su da Afrika.Tallafin da suke baiwa ƙasashen Afrika irin na sha yanzu biya yanzu, saɓanin Amurika da Turai, inda sai an jima ana tafka dogon turanci, tare da gitta sharuɗan da sai ƙasa ta cika su.

Hatta cikin 'yan kwanakin nan ,Amurika ta yanke shawara dakatar da taimakawa Ruwanda dalili da zargin da ta ke wa gwamnatin Kigali na haɗa kai ada 'yan tawaye domin tada fitina a Jamhuriya Demokraɗiyar Kongo.

Philipp Gieg manazarcin al'amuran siyasar ƙasa da ƙasa ne a jami'ar Würzburg dake nan Jamus wanda a tunaninsa akwai kura-kurai da muna-muna a cikin ma'amala tsakanin Amurika da Afrika kuma ya bada hujjoji:

"Amurika na matsa ƙaimi ga ƙasashen Afrika, game da wajibcin tabbatar da demokraɗiyya da kare 'yancin bani Adama, to amma ta nuna bambanci a cikin al'amarin,ɗauki misali da ƙasar Ethiopiya wadda ta yi ƙaurin suna ta fannin take haƙƙoƙin jama'a da kuma tauye demokraɗiyya, amma Amurika ba ta taba daga yatsa ba domin tsawatama hukumomin ƙasar."

Chinese President Hu Jintao, front right shake hands with Ethiopia's Prime Minister Meles Zenawi at front left and other African leaders look on at the end of the Forum on China-Africa Cooperation held a the Great Hall of the People in Beijing, China, Sunday, Nov. 5, 2006. China and Africa ended an unprecedented summit Sunday, signing deals worth US$1.9 billion (euro1.49 billion) and pledging to boost trade and development between the world's fastest-growing economy and its poorest continent. (AP Photo/Ng Han Guan)
Shugaban China Hu Jintao na ganawa da wasu shugabanin ƙasashen AfirkaHoto: AP

Bincike da wata cibiyar nazari ƙungiyar tarayya Turai ta gudanar ya gano cewar Afrika na cin moriyar kashi 46 cikin ɗari na kuɗaɗen taimakon raya ƙasa da China ke kashewa ko wace shekara, ta fannin gine-ginen hanyoyi asibitoci makarantu da dai sauran aiyukan cigaban ƙasa.

Mawallafi:Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Umaru Aliyu