1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hausawan Sudan sun yi tir da kabilanci

Mouhamadou Awal Balarabe
July 19, 2022

Daruruwan Hausawa sun taru a birnin Khartoum a wannan Talata domin yin tir da rigingimun kabilanci tsakaninsu da kabilar Bartis wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane 79 a karshen makon jiya.

https://p.dw.com/p/4ELtR
Sudan - Proteste von Gegnern der Militärjunta in Khartoum
Hoto: Marwan Ali/AP

Galibin masu zanga-zangar na dauke da allunan da ke neman a kawo karshen kashe-kashen Hausawa, yayin da wasu ke jinjina wa wadanda tashin hankalin ya ritsa da su. Wannan rikici kan kasa tsakanin Hausawa da kabilar Bartis- ya barke ne a ranar Litinin din da ta gabata a jihar Blue Nile da ke kan iyakar Sudan da kasar Habasha.

Duk da cewa hankali ya kwanta a wannan yanki, amma rikicin ya bazu zuwa wasu jihohi da dama na Sudan da suka hada da Kassala da ke Arewa, inda a ranar Litinin dubban Hausawa suka kona wasu gine-ginen gwamnati. Dama dai rikicin ruwa da filayen noma sun jima suna sanadin mutuwar daruruwan mutane a kasar Sudan.