1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gommai sun mutu a hatsarin jirgi a Indiya

Zainab Mohammed Abubakar
June 2, 2023

Gomman mutane sun rasa rayukansu kana wasu 200 sun jikkata sakamakon wani hatsarin jirgin kasa da ya afku a gabashin jihar Odisha a kasar Indiya.

https://p.dw.com/p/4S8o2
Train accident in Balasore, India
Hoto: ANI/Reuters

Shaidun gani da ido da jami'ai sun shaidawa kafafen yada labarai na cikin gida cewa, jirgin fasinja na Coromandel Express da wani jirgin dakon kaya sun yi karo a kusa da Balasore mai tazarar kilomita 200 daga Bhubaneswar babban birnin jihar.

Kazalika hatsarin ya kuma ritsa da wani jirgin fasinja na biyu, a cewar babban sakataren Odisha Pradeep Jena, amma har yanzu ba a fayyace yadda lamarin ya kasance ba.

Sai dai wasu jami'ai da ba a bayyana sunayensu ba sun ce kimanin mutane 50 ne ake fargabar sun mutu, a yayin da wasu fasinjoji da yawa ke makale a karkashin jirgin dakon kayan.

Ofishin mataimakin sufeto janar na ‘yan sandan Balasore ya shaidawa kamfanin dilancin labaren AFP cewa akalla mutane 200 ne sun jikkata, kuma yawancinsu munanan raunuka.