1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan ta'adda sun hallaka sojojin Burkina Faso

Abdoulaye Mamane Amadou
May 12, 2020

Wasu sojojin Burkina Faso hudu sun halaka a yayin wani harin da ake kyautata zaton mayakan jihadi ne suka kai shi a yankin arewacin kasar mai iyaka da Jamhuriyar Nijar.

https://p.dw.com/p/3c3vB
Symbolbilder Niger Armee
Hoto: picture-alliance/Zumapress/D. White

Rahotanni daga Kankanfogouol da ke arewacin Burkina Faso sun yi nuni da cewa kimanin sojojin kasar hudu ne suka halaka a yayin da wasu kuma hudun suka yi batan dabo sakamakon wani harin kwantar bauna da mayakan jihadi suka yi wa ayarin sojan kasar da ke sintiri a yankin da ke kan iyaka da Jamhuriyar Nijar.

Wata majiyar tsaron kasar ta tabbatar da harin tare da bayyana cewa tuni dakarun rundunar sojan kundun balar kasar ta kaddamar da wani samame domin kakkabe mayakan da suka kai harin.

Ba tun yau ba dai kungiyoyi masu tayar da kayar baya ke labawa da yankin suna kai hare-haren ta'addanci  a tsakanin kasashen biyu na Nijar da Burkina Faso.