1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Tsageru sun halaka sojojin Burkina Faso 12

Suleiman Babayo LMJ
October 4, 2021

Sojojin Burkina Faso 12 suka halaka sakamakon hari da ake dangantawa da kungiyoyin jihadi a yankin arewacin kasar.

https://p.dw.com/p/41Fj7
Symbolbild I Sicherheitskräfte Burkina Faso
Hoto: Ahmed Ouoba/AFP/Getty Images

Sojojin Burkina Faso 12 suka halaka yayin da wasu biyar suka jikata sakamakaon harin tsageru masu dauke da makamai a yankin arewacin kasar. Majiyoyin tsaron kasar sun tabbatar da cewa an kai harin a wannan Litinin.

Galibin wannan hare-hare da kasar ta Burkina Faso da ke yankin yammacin Afirka ke fuskanta ana dangantawa da tsageru masu kaifin kishin addinin Islama.