1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Hari ya halaka mutane uku a Somaliya

Suleiman Babayo MAB
March 15, 2024

Hukumomin Somaliya sun tabbatar da mutuwar mutane uku kana wasu kusan 30 suka jikata a harin da tsageru suka kai a kasar mai fuskantar tashe-tashen hankula.

https://p.dw.com/p/4deDM
Somaliya inda tsgeru suka kai hari
Somaliya inda tsgeru suka kai hariHoto: Farah Abdi Warsameh/AP Photo/picture alliance

Mutane uku suka halaka yayin da wasu kusan 30 suka jikata sakamakon harin da aka kai kan wani otel a birnin Mogadishu fadar gwamnatin Somaliya cikin dare, kamar yadda mai magana da yawun 'yan sanda ya tabbatar.

Tuni jami'an tsaro suka yi kawanya ga wannan otel da jami'an gwamnati ke amfani da shi, kuma tuni tsagerun kungiyar al-Qeada suka dauki alhakin kai harin na Somaliya.