1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hari kan jami'an tsaro a Burkina Faso

Binta Aliyu Zurmi
November 15, 2021

Rahotanni daga Burkina Faso na nuni da cewar wani harin ta'addanci da aka kaddamar a kan jami'an tsaro da farar hula ya yi sanadiyar mutuwar akalla mutum 19 a cewar ministan tsaron kasar Maxime Kone.

https://p.dw.com/p/42zdI
Burkina Faso Symbolbild Anschlag
Hoto: Str/AFP

Sai dai wasu jami'an tsaro sun ce adadin ya kai 30 kuma akwai yiwuwar ya karu, wanda ake gani shi ne hari mafi muni a kan 'yan sanda.

Harin da aka kaddamar da shi a ranar Lahadi, ya auku ne a wani wurin bincike na 'yan sanda da ke kusa da mahakar zinari a garin Inata da ke arewacin Burkina, wannan harin na zuwa ne kwanaki biyu bayan da wani makamancinshi ya kashe 'yan sanda bakwai a kan iyakokin Nijar da Mali.

'Yan ta'adda da suka yi mubaya'a da kungiyar al-Qaeda da ta IS sun jima suna aikata ta'asa a iyakokin kasashen Burkina Faso Nijar da Mali duk da sojojin kawance da na kasar Faransa da ke yankin.