1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaSudan

Hari kan dam na barazanar haddasa ambaliyar ruwa a Sudan

Mouhamadou Awal Balarabe
November 18, 2023

Sojojin da ke biyeyya ga gwamnatin Sudan da kuma dakarun sa-kai na RSF sun zargi junansu da kai harin da ya lalata gada ta madatsar ruwan Jebel Awlia da ke kudancin birnin Khartum.

https://p.dw.com/p/4Z8AU
Irin wannan madatsar ruwan Merowe ne ake kai wa hari a kudancin khartum
Irin wannan madatsar ruwan Merowe ne ake kai wa hari a kudancin khartumHoto: picture-alliance/Photoshot

Har yanzu ba a tantance girman barnar da aka yi a madatsar ruwan ba, amma dai tana barazanar haddasa ambaliya ruwa. A baya-bayan nan, fada ya karu a yankin Jebel Awlia wanda ya yi sanadin raba dubban mutane da matsugunansu, a wannan gunduma mai fama da talauci a kudancin lardin Khartum.

A farkon wannan watan ne, dakarun RSF ta mataimakin shugaban kasar Mohammed Hamdan Daglo ta ce ta kama wani sansanin sojoji a yankin. Sannan a cikin 'yan makonnin da suka gabata, an lalata wata gada a babban birnin kasar Khartum tare da lalata wata muhimmiyar ma'ajiyar man fetur a hare-haren da bangarorin biyu ke zargin junansu da kaiwa.