1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wani sabon hari a birnin Khartoum ya hallaka gwamman mutane

Binta Aliyu Zurmi
June 17, 2023

Ma'aikatar lafiya a kasar Sudan ta ce wani sabon hari ta sama da aka kai a yau Asabar a birnin Khartoum ya yi sanadiyar rasuwar fararen hula 17, wanda 5 daga cikinsu yara ne kanana.

https://p.dw.com/p/4SicU
Sudan Karthoum | Unruhen: Ausgebranntes Auto
Hoto: EL TAYEB SIDDIG/REUTERS

Harin wanda aka kai yankin nan na Yarmouk ya kuma lalata gidaje 25 duk a cewar sanarwar.

Can ma a yankin Darfur, ma'aikatan jinya na kokawa da yawan mutanen da ke jikkata a cigaba da kwabza kazamin fada da bangarorin da ke gaba da juna ke yi a kasar.

Adadin mutanen da suka rasu a yakin tun bayan barkewarsa a tsakiyar watan Afirilu ya haura mutum dubu 2.