1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar NATO EU sun sanar da hadakar tsaro

Zainab Mohammed Abubakar
January 11, 2023

Kungiyar tsaro ta NATO da tarayyar Turai sun ba da sanarwar wani hadin gwiwa da nufin karfafa kariya ga muhimman wurare dangane da barazanar da suke fuskanta daga kasar Rasha.

https://p.dw.com/p/4M14r
Belgien Brüssel | NATO-EU Gipfeltreffen - Jens Stoltenberg und Ursula von der Leyen
Hoto: Dursun Aydemir/AA/picture alliance

Matakin na zuwa ne bayan wani hari da aka kai kan bututun iskar gas na karkashin ruwa na Nord Stream a bara da kuma yadda kungiyoyin biyu ke neman karfafa hadin gwiwa a sakamakon mamayar da Rasha ta yi a Ukraine.

Shugabar hukumar gudanarwa ta tarayyar Turai Ursula von der Leyen ta ce rundunar za ta hada kwararru na EU da NATO don yin nazari kan raunin muhimman wuraren, tare da ba da shawarar hanyoyin da za a kare su.

A wata ganawa da babban sakataren kungiyar NATO Jens Stoltenberg a Brussels na Belgium,  von der Leyern ta ce sun ga irin zagon kasa da aka yi a kan Nord Stream, wanda ya nuna cewa akwai bukatar kasancewa cikin shirin ko ta kwana na tunkarar wannan sabuwar barazana.