1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Firaministan Habasha na ziyarar aiki a Afirka ta Kudu

Zulaiha Abubakar
January 12, 2020

Firaministan kasar Habasha Abiy Ahmed ya bukaci shugaba Cyril Ramaphosa na kasar Afirka ta Kudu ya sanya baki a rikicin kasashen kan batun tekun Nilu.

https://p.dw.com/p/3W5Zg
Friedensnobelpreis 2019 Äthiopien | Ministerpräsident Abiy Ahmed
Hoto: Getty Images/AFP/E. Soteras

Firaminista Ahmed na Habasha din ya mika wannan bukata ce yayin da yake ziyarar aiki a kasar Afrika ta Kudu a wannan Lahadin, ya kuma kara jaddada muhimmancin shigar Afirka ta Kudu cikin batun a daidai lokacin da ake dab da nada sabon shugabancin kungiyar AU.

Tsamin dangantakar Habasha da Masar dai ya samo asali ne a shekara ta 2011, bayan gwamnatin Habasha ta kaddamar da shirin samar da wata cibiyar ruwa domin samar da hasken wutar lantarki irin sa na farko a nahiyar Afrika.  Al'amarin da ya sanya mahukuntan Masar zargin Habasha da yunkurin haifar da koma baya a harkokin samar da wadataccen ruwa a fadin kasar.