1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Girka sabuwar Majalisar Wakilai ta Libiya

August 8, 2012

Gwamnatin wucin gadi ta Libiya ta miƙa mulki ga sabbin wakilan majalisar da aka zaɓa a cikin watan Yuli da ya gabata

https://p.dw.com/p/15lj8
Der Vorsitzende des libyschen Übergangsrates, Mustafa Abdul Dschalil, spricht am Montag(19.04.2011) bei einer Pressekonferenz im italienischen Außenministerium in Rom. Dschalil habe die Zahl der Opfer bei dem Auftstand gegen das Gaddafi-Regime erneut auf 10 000 beziffert und von bis zu 55 000 Verletzten gesprichen, sagte der italienische Außenminister Franco Frattini nach dem Treffen mit Dschalil. Italien hatte Anfang April angekündigt, den Übergangsrat der Anti-Gaddafi-Rebellen als einzigen Gesprächspartner formal anzuerkennen. Foto: Mauro Scrobogna /LaPresse dpa (zu dpa 0683) +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture-alliance/dpa

An shirya shugaban gwamnatin riƙon ƙwarya Mustafa Abdeljalil zai miƙa iko ga sugaban wuccin gadi yan majalisar mai wakilai 200 wacce za ta kula da rubuta sabon kudin tsari mulki na ƙasar da zai kai ga shirya wasu zaɓbuƙa bisa ta farki na dimokaradiyya.

Tun da farko jama'a sun yi ta yi mamaki dangane da sakamakon zaɓen yan majalisun wanda shi ne karo na farko da aka gudanar a cikin shekaru goma wanda ya kai ga bai wa ƙawancen jam'iyyun siysar masu sasaucin ra'ayi ta tsohon framinista Mahmud Jibril samun rinjaye a zaɓen

An dai yi tsamanin ga irin abinda ya faru na juyin juya hali a cikin wasu sauran ƙasashen larabawar, masu kishin adinnin islamar zasu yi galaba a zabe to amma sai abin ya sha banban.

Ana tsamani samun wani sabon ƙawance a cikin majalisar

Du dama yadda majalisar ta wakilai ta kasu a kaso daban daban na jam'iyyun siyasar da kuma yan takara indepanda ,babban abinda ake jira ga majalisar shi ne na rawar da zata taka ga ƙasar da ta yi fama da juyin juya halin da ya kawo ƙarshen mulkin kama karya na kanal Gaddafi na kusan shekaru 40 domin sake samun yardda jama'a tare da dawo da kwanciyar hankali da kuma doka a oda.Kurt Pelda wani ƙwarrare akan Libiya ya shaida wa DW cewar saɓanin da ke tsakanin yan siyasar ba zai hanna su ba yin hulɗa ba ''ya ce mai yiwa ne masu kishin islama su shawo kan yan indepanda domin taka wata muhimiyar rawa a majalisar don yin wani ƙawance.

Libyan National Transitional Council (NTC) Chairman Mustafa Abdel Jalil (C) speaks during a news conference in Tripoli April 29, 2012. Libya's ruling National Transitional Council (NTC) decided on Sunday to keep the interim government in power in the run up to a June election, its leader said, quashing rumours of a reshuffle that has sowed uncertainty in the strife-torn state. REUTERS/Ismail Zitouny (LIBYA - Tags: POLITICS)
Shugabannin gwamnatin riƙon ƙwarya na LibiyaHoto: REUTERS

A na tuanani cewar majalisar za ta yi kokarin magance irin mumunar abubuwan da aka yi fama da su a zamanin mulkin kama karya ; wanda a ƙarƙashin mulkin Gaddafi wanda ya fara mulki tun a shekara ta 1969 yankin Syrte inda nan ne maihafarsa da Tripoli suka fi cin moriyar arzikin man fetir da ƙasar ta ke da shi , kuma sauran yankuna sun yi ta fama da wahaloli, ''ya ce a zamani mulkin Gaddafi ababan da suka shafi hanyoyi da titina da sauran kayayakin gine gine an yi sakaci akan su, ya a ce a yanzu aikin fitar da ɗanya man fetir ɗin ya na tafiya da kyau, sai dai babu gyara na kayayakin da ake yi abinda ka iya zama babbar matsala a gaba inda ba a ɗauki mataki.

Brazanar ga taɓarɓarwar al'amuran tsaro

Fighters prepare for clashes between rival militias in the southern Libyan city of Sabha March 28, 2012. Picture taken March 28, 2012. REUTERS/Ibrahim Azagaa (LIBYA - Tags: POLITICS CIVIL UNREST CONFLICT)E DAY CONFLICT)
Mayaƙan da ke riƙe damakamaiHoto: Reuters

A yankunan da dama na ƙasar Libiya ɓangarorin al 'umma daban daban ko wane na da nasa mayaƙan sa kai dole ne sai gwanatin ta kirshe domin tabbatar da tsaro .Abinda ake ganin babban ƙalubale ne dake a gaban sabuwar majalisar shine na kawance ɗamarar mayaƙan kamar yadda wani dan jarida Laswad ya baiyana wa DW ''ya ce maganar tsaro a Libiya wani abu ne da ke da mahimanci a yanzu ya ce a kwai gomai na duban jama'a da ke ɗauke DA makamai waɗanda ba su cikin ƙaida ya ce ƙwance ɗamarar' waɗannan mayaƙa shi ne babban tushen tabbatar da tsaro.

Na gaba ne dai inda sun fara zaman taron sabbin yan majalisar na CGN zasu zaɓi shugaba da wasu mataimaka guda biyu ,a lokaci ne kuma za a rusa gwamnatin wucin gadin ta CNT: za dai a gudanar da taro majalisar ne a cikin tsatsauran matakan tsaro a daidai lokacin da rahotanni ke ambato cewar an kama wasu mutane guda ukku a cikin wannan mako a birnin Tripoli waɗande ƙoƙarini tayar da bama bamai.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Yahouza Sadissou Madobi

Daga ƙasa za a iya sauran wannan rahoto